Surah Al-Qamar Translated in Hausa
![](https://www.al-quran.cc/images/pictures/surah/bismillah.png)
وَإِنْ يَرَوْا آيَةً يُعْرِضُوا وَيَقُولُوا سِحْرٌ مُسْتَمِرٌّ![](https://www.al-quran.cc/images/pictures/ayah_num/a_2.png)
![](https://www.al-quran.cc/images/pictures/ayah_num/a_2.png)
Kuma idan sun ga wata ãyã, sai su juya baya su ce: "Sihiri ne mai dõgẽwa!"
وَكَذَّبُوا وَاتَّبَعُوا أَهْوَاءَهُمْ ۚ وَكُلُّ أَمْرٍ مُسْتَقِرٌّ![](https://www.al-quran.cc/images/pictures/ayah_num/a_3.png)
![](https://www.al-quran.cc/images/pictures/ayah_num/a_3.png)
Kuma suka ƙaryata, kuma suka bi son zũciyarsu, alhãli kuwa kõwane al'amari (wanda suke son su tũre daga Annabi) an tabbatar da shi.
وَلَقَدْ جَاءَهُمْ مِنَ الْأَنْبَاءِ مَا فِيهِ مُزْدَجَرٌ![](https://www.al-quran.cc/images/pictures/ayah_num/a_4.png)
![](https://www.al-quran.cc/images/pictures/ayah_num/a_4.png)
Kuma lalle, abin da yake akwai tsãwatarwa a cikinsa na lãbãraiya zo musu.
حِكْمَةٌ بَالِغَةٌ ۖ فَمَا تُغْنِ النُّذُرُ![](https://www.al-quran.cc/images/pictures/ayah_num/a_5.png)
![](https://www.al-quran.cc/images/pictures/ayah_num/a_5.png)
Hikima cikakka! Sai dai abũbuwan gargaɗi bã su amfãni.
فَتَوَلَّ عَنْهُمْ ۘ يَوْمَ يَدْعُ الدَّاعِ إِلَىٰ شَيْءٍ نُكُرٍ![](https://www.al-quran.cc/images/pictures/ayah_num/a_6.png)
![](https://www.al-quran.cc/images/pictures/ayah_num/a_6.png)
Sabõda haka, ka bar su! Rãnar da mai kiran zai yi kira zuwa ga wani abu abin ƙyama.
خُشَّعًا أَبْصَارُهُمْ يَخْرُجُونَ مِنَ الْأَجْدَاثِ كَأَنَّهُمْ جَرَادٌ مُنْتَشِرٌ![](https://www.al-quran.cc/images/pictures/ayah_num/a_7.png)
![](https://www.al-quran.cc/images/pictures/ayah_num/a_7.png)
¡asƙantattu ga idanunsu zã su fito daga kaburburansu, kamar dai sũ fãri ne waɗandasuka wãtse.
مُهْطِعِينَ إِلَى الدَّاعِ ۖ يَقُولُ الْكَافِرُونَ هَٰذَا يَوْمٌ عَسِرٌ![](https://www.al-quran.cc/images/pictures/ayah_num/a_8.png)
![](https://www.al-quran.cc/images/pictures/ayah_num/a_8.png)
Sunã gaggãwar tafiya zuwa ga mai kiran, kãfirai na cẽwa, "Wannan yini ne mai wuya!"
كَذَّبَتْ قَبْلَهُمْ قَوْمُ نُوحٍ فَكَذَّبُوا عَبْدَنَا وَقَالُوا مَجْنُونٌ وَازْدُجِرَ![](https://www.al-quran.cc/images/pictures/ayah_num/a_9.png)
![](https://www.al-quran.cc/images/pictures/ayah_num/a_9.png)
Mutãnen Nũhu sun ƙaryata, a gabãninsu, sai suka ƙaryata BawanMu, kuma suka ce: "Shi mahaukaci ne." Kuma aka tsãwace shi.
فَدَعَا رَبَّهُ أَنِّي مَغْلُوبٌ فَانْتَصِرْ![](https://www.al-quran.cc/images/pictures/ayah_num/a_10.png)
![](https://www.al-quran.cc/images/pictures/ayah_num/a_10.png)
Sabõda haka, ya kira Ubangijinsa (ya ce), "Lalle nĩ, an rinjãye ni, sai Ka yi taimako."
Load More